RAYUWAR `YAN MATA
A JAMI`A
Dasunan Allah mai rahama mai jin
ƙai, mamallakin sammai da ƙassai.
Inaso a cikin damar da Allah
ubangiji ya bamu na mallakar wannan kafa mai Albarka nadan dangwali tawada
domin tofa Albarkacin baki akan irin Rayuwa mai tarin sarƙaƙiya wato RAYUWAR
`YAN MATA A JAMI`A .
Tabbas wannan Al`amari babba ne,
kuma abin a tausayawa wadanda abin ya shafa ne, kuma tabbas idan har kana da
kishi da tausayi koda gwargwadon kwayar zarra a cikin zuciyarka matukar kasan
ire-iren abunda ke faruwa lallai zaka tausaya.
Mace a Jami`a tamkar Yankan nama ne
a tsakanin kuraye a yayin da kowacce yunwa ta isheta, zaka iya yarda da
maganata idan
kayi duba na basira ga rayuwar da suke gudanarwa acan, BA INA SUKAR KARATUN MACE BANE A JAMI`A ina kokarin naga na saka tausayinsu a zuciyar Al`ummah ne.
kayi duba na basira ga rayuwar da suke gudanarwa acan, BA INA SUKAR KARATUN MACE BANE A JAMI`A ina kokarin naga na saka tausayinsu a zuciyar Al`ummah ne.
Mace kadai ce a jami`a zaka ga tana
da kalubale ta kowane bangare. Ta bangaren dalibai `yan uwanta akwai course
mate wanda mafi yawanci sunanan suna kyalla
ido suga wacece kyakkyawa su makale mata, ba batun soyayya ne ya kawo su
gurinta ba, ba kuma Al`Amari na karatu ba, ba `yar uwar su ce ba, a a kawai
saboda chilling ko flexing wato su kawai su jero da ita ace wancan ya cinye
kawai abinda sukeso Kenan, wasu ko `yan bata tarbiyya ne kawai suga sun lalata
yarinya ba don suma su Aureta ba za dai tasha karya ne kawai sudai kawai `yan
soyayya dadine. Akwai `yan uwanta mata kuma musamman idan tana da kokari tabbas
zata sha hassada daga garesu, abin dubawar anan shine itafa jami`a ba makaranta
ce da za`a ce wane yaci na daya ko wane yaci na karshen aji bane ballantana ace
ai saboda ta wuce watane ko kuma sunyi kankankan to amma bansan abinda ke kawo
wannan hassadar ba, idan kuwa akai rashin sa`a ta kasance cikin wadanda basu da
kokari tofa tabbas izgili da wulakanci su zasu dinga take mata baya. Babban
abinda yafi komai muni kuma shine harin da `yan mata yan maƌigo suke kaiwa
musmman wadanda suka ga cewa salihan bayi ne, wannan ƙazamar ƌabi`a ta yawaita
musamman ga `yan mata masu zama a hostels( bance duka ba), ta inda zakaga mace
na neman `yar uwarta mace iyazan billah wato lesbianism. Akwai kuma Musibar da
tafi kowace ban tsoro
ita musibar Cultism wacce ta zama ruwan dare zagaye
duniya, wanda wannan shine mafi girman kalubale ga daliban jami`a( matan da
mazan) musamman `yan ajin farko, kodai sum aka tayi ka karba kokuma suyi maka
barazanar mutuwa wanda ta dalilin hakan wasu da dama ke afkawa wannan sharri
domin basa so su mutu ( saidai sun manta Allah shike kashewa da rayawa a duk
lokacin daya so), sukanyi Al`bishir ga duk wanda ya karba cewa zasu inganta
rayuwarsa ta hanyar sanyashi cin jarabawa koda bai yi karatu ba kokuma suyi baerazanar hana ka cin
jarabawar idan ka ki. Idan kuma mace ta samu ta tsallake wadancan matsaltsalu
akwai wata gagaruma kuma wannan itace gurbatattun lecturers wadanda su kuma
burinsu shine mace ta yarda ta basu hadin kai su kuma su bata maki koda kuwa
bata cancanci wannan maki ba idan kuwa akai rashin sa`a taki amincewa da
bukatarsu to zasu san duk yadda zasuyi suga sun kada ita koda kuwa tafi kowa
kokari, babu ruwansu da ita din mai kamun kaice kokuma fitsararriya, `yar
talaka ce ko kuma `yar mai kudi, musulma ce ko kafira sudai mace dai mace,
rashin tsoron Allah kuwa ba`a Magana domin duk irin hadashi da Allah da zatayi
shi ko ajikinsa ballantana ya saduda. A gida kuma iyaye na jira ne ta kawo musu
good result wanda shima kalubale ne a gareta, ga Al`ummar unguwa wasu kallon
yan jami`a kawai suke a matsayin yan tasha duk sanda aka ce wance `yar jami`ace
to kallon mutunci kuwa raguwa yake a idon jam`a, ga uwa uba samari masu neman
Aure ba kasafai suke Auren `yan jami`a ba muamman wadanda suma sukai jami`ar
badon kome ba hujjar su kawai bata wuce tantamarsu akan anya ta tsallake
wadancan matsaltsalu na sama? Bayansu akwai bata gari na cikin Al`ummah wadanda
su kuma aikinsu shine shiga jami`a musamman da yammaci domin zabo `yan mata a
tafi outing dasu, sannan kuma su dawo gida a zauna dasu anan zagin su `yan
matan.
Duk wadancan matsaltsalu kuma akwai
shedan shikuma a gefe yana nan yana dubawa duk wacce ta kauce wa laifi sai
yasan yadda yayi ya saita ta ta tafi akan Alkawarin da yayi wa Allah sedai idan
ta kasance daga cikin bayin Allah na kwarai.
Meye mafita?
Ni a ganina mafita bata wuce
lizimtar roƙon ubangiji tare da dogewa kan koyarwar Annabin rahama (Annabi
Muhammad ﷺ ) bisa ga tafarkin magabata na kwarai.
Shawara ga `yan mata
Shawarar da zan iya ba `yan
mata wadanda suke ciki da wajen Jami`a shine kuji tsoron Allah wanda ya
halicceku, duk abinda kuka aikata a fili ko a boye to tabbas yana kallonku
domin shi babu wani abu dake iya buya daga gareshi, kuma a ranar da kowace gaba
zatayi Magana zai tambayeku akan abin da kuka kasance kuna aikatawa a rayuwarku
ta duniya. Sannan ya kamata ku sani duk wata irin kima da mace keda shi to yana
cikin hijabinta na mutunci a duk lokacin da wannan hijabi ya yaye to ita mace
bata da wani sauran kima a idon kowaye koda kuwa shine wanda ya taimaka mata
wajen cire wannan hijabin mutuncin, domin shi kallon out dated yake mata, don
haka a matsayinki na mace ki kare mutuncinki da na gidanku shi yafi. Allah yasa
mu dace.
Shawara ga iyaye
Kun fini sanin irin kuncin da
kuke shiga idan kuka ga `ya`yanku sun lalace, domin kuwa sakamakon hakan kanku
yake fara komawa, duk wani mai zargi bazai taba zargin `yar a matakin farko ba
sai ya dangana da irin tarbiyyar da kuka bawa `yar ko da kuwa kunyi iya bakin
kokarinku wajen ganin kun saita ta a kan tafarki madaidaici.
Shawarar da zan baku dai bata
wuce sa ido da dogewa wajen tabbatar da `yarku tana da kawaye na gari, domin
babu abu mai canza tarbiyyar mutum a lokaci guda irin Aboki, zaku iya ku dauki
fiye da shekara goma sha takwas kuna gina ma `yarku matakalar takawa domin zuwa
tudun mun tsira amma a cikin dakiku kadan sai kawa mara tsoron Allah ta
rusheshi. Zabarwa `ya`ya uwa ta gari da uba nagari yana matukar taka rawar gani wajen taimakawa
`yarku ta zamto ta kirki.
Babban ginshiƙi kokuma ince
gadon baya shine Addu`a, domin kwarai da gaske Al`amarin Tarbiyya saida Addu`a.
Abin lura
Duk wadancan Abubuwanda na lissafo wadansu na gani
da idona wadansu kuw naji labari daga majiya mai karfi, dukda cewa har yanzu
ban gama sanin sauran matsaltsalun ba. Wadansu kalmomin danai Amfani dasu kuwa
na jami`ar ne sakamakon zama da ma`a bota su.
Bana nufin kowace jami`a haka
take amma tabbas mafi yawanci suna tattare da wadannan abubuwa masu matukar
rikitarwa. Mai karatu kaima nasan zaka iya sanin wadan su matsalolin ba
wadannan ba , idan kuma kanada shawara zaka iya comment da taka shawarar mudai
fatanmu shine a gyara.
Muna fatan Allah ya shiryar
damu da kuma zuriyarmu baki daya .
Da wannan ni AHMAD ABDULKAREEM AL-ABSHATY nake cewa:
الزرع إن طاب يُحصد ذاك قيمته** والكفّ في ذا طبيب فاته العقل
No comments:
Post a Comment